Home

Music

Video

Kanny

Dalilin da ya sa nake bangaren wasan barkwanci — Dangwari



Shahararren jarumin nan mai wasan barkwanci a dandalin shirya fina-finan Kannywood, Muhammadu Sani Ibrahim Tsiga wanda aka fi sani da Dangwari ya bayyana dalilan da su ka sa ya rungumin bangaren barkwanci. A cewar jarumin, marigayi Rabilu Musa (Dan Ibro) shine ya sa masa sha’awar shiga wasan fina-finan Hausa.
Jarumin ya kasance dan asalin jihar Katsina kuma haifafan jihar Kaduna.
A cewarsa marigayi Dan Ibro ne ya karfafa masa gwiwar kwaikwayon gwari domin a cewar sa babu mai wannan baiwar ta kwaikwayon gwarawa a fim. Wato kenan kwaikwayon gwarawa ya zame masa jari.
Dangwari ya bayyana cewa ya so ya bar harkar fim a lokacin da labarin rasuwar Dan Ibro ya riske shi amma sai ya ga haka Allah ya tsara don haka ya ci gaba da sana’ar ta sa.,

Share this



Fb tt wp ig
Powered by DailyBookNg and Developed By Emranjega