Shugabannin APC na jihohin Yarbawa sun nuna cewa Shugaba Muhammad Buhari bai sanar da su cewa zai sake tsayawa takara a karo na biyu ba don haka a cewarsa, kofa bude take ga duk wanda ke sha'awar neman kujerar shugabancin kasar a karkashin APC. Tsohon Shugaban riko na APC, Bisi Akande ne ya yi wannan ikirarin bayan wani taro da suka yi a Ibadan wanda ya samu halartar jigogin jam'iyyar da suka da gwamnonin Oyo, Mista Abiola Ajimobi, Akinwunmi Ambode (Lagos), Ogbeni Rauf Aregbesola (Osun), Ibikunle Amosun (Ogun), Rotimi Akeredolu (Ondo), former governors; Adebayo Alao-Akala (Oyo), Olagunsoye Oyinlola (Osun), Olusegun Osoba (Ogun), Adeniyi Adebayo (Ekiti), Kayode Fayemi (Ekiti).



