Shahararren Sojan Bakan Siyasa a jihar Kano, Abdulmajid Dan Bilki Kwamanda, wanda ya shahara wajen kare manufofin gwamnatin Muhammadu Buhari. Ya yi addu'ar duk inda Allah zai sa Buhari ranar lahira shima a sa shi. Kwamanda ya furta wannan furuci ne a wani gidan Radiyo mai zaman kansa jiya a jihar Kano. 'Yar jaridar ta ja hankalinsa da cewa, "Duk fa inda Allah Ya sa Buhari ka ce?" sai ya amsa da cewa, "Duk inda Ya sa shi nima ya sa ni, a garin nan akwai wanda ba mutumin kirki ba ne amma an fadi abinda ya fi haka a kansa".
Daga jaridar mikiya Facebook



