Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya yi wa al'ummar kasar jawabi a safiyar ranar Litinin kwana biyu bayan komawarsa kasar.
A jawabin mai tsawon minti 5.40, shugaban ya yi godiya ga 'yan kasar bisa ga addu'o'in da suka yi masa yayin da shafe kwana 103 yana jinya a birnin Landan.
Har ila yau shugaban ya mayar da martani ga masu fufutikar ballewa daga kasar da batun tsaro da kuma gyara tattalin arzikin kasar.
Sai dai shugaban bai yi karin haske ba kan batun lafiyarsa.
Zan yaki 'yan ta'adda da miyagu – Buhari
Share this
|
|




